Labarai
Kungiyoyi sun yi zanga-zanga a Kano

Gamayyar kunigiyo masu zaman kansu a nan jihar Kano sun gudanar da zanga-zangar lumana yau juma’a a nan Kano domin nuna takicinsu kan yadda yan jaridu suka yi shiriu da batun yaran da aka sace a ka kai jihar Anambra aka kuma mayar da su kirista.
Gamayyar kungiyoyin sun yi tattakin ne yau a nan Kano inda suke dauke da rubutu da ke nuna yin Alawadai da al’amarin tare da zarigin yan jaridu da kuma gwamnati da yin guma da bakin su.
Guda daga cikin masu zanga-zangar Shazali Abubakar Adamu ya shaidawa freedom Radio cewar sun fito zanga-zangar ne domin nuna adawa da satar yaran aka kuma mayar da su kirista, amma gwamnatoci suka yi shiru.
Satar yaran Kano da munafurcin kafafan yada labarai
Yaran Kano: Majalisar dokokin Kano zata dauki mataki
An siyar da ‘ya ta naira Miliyan Daya da rabi
Shima da yake nasa jawabin ga dandazon masu zanga-zangar Bashir Usaini kira yayi da babbar murya ga mahukunta da su fito su magantu su kuma dauki matakin gaggawa kan al’amarin
Haka shima Sagiru Alhansan ya kalubalanci kafafen yada labarai da sauran jama’ar gari kan nuna halin ko in kula da jama’a sukayi kan al’amarin yana mai cewar abu ne da yakamata jama’a su hada hannu wuri guda.
Kungiyoyi da dama ne dai suka fito daga nan jihar Kano suka kuma hadu wuri guda domin gudanar da zanga-zangar ta lumana damin jan hankalin gwamnati da ta mayar da hankali kan al’amari.
Inda Ranka
Kotu ta saida gidan wani mutum yana gidan gyaran hali

Duk da cewar bayan ya fito ya kai shigar da kara har ma kotu ta bada umarni amma hakonsa bai cimma ruwa ba, domin masu gwanjan babbar kotun jiha sun bujirewa umarnin ta
Wakilin mu Nasiru Salisu Zango ya rawaito cewa, a cikin kunshin bayanan shari’a wanda alkali Faruq na kotun kasuwa ya rubuta ya nuna cewa, irin hukunce-hukuncen da kotun ta bada umarni amma wadanda ake kara suka yi mirsisi a don haka kotun ta bayyana cewar matakin ya zama rainin-wayo.
Kamar yadda labarin ya nuna cewa wani mutumi ne wanda karayar arziki ta same shi har ta kai ga cin bashin da aka kai shi kurkuku saboda ya gaza
Wanda yana cikin wannan kadamin ne sai aka sake kai karar sa kotun kasuwar Kurmi saboda wadansu kudadan da ake binsa,duk da cewar an je wannan kotun kasuwar don tabbatar da sulhun da aka cimma a tsakanin su kama yadda hukuncin kotun ke tafiya akai, amma sai shari’ar ta sauya zane daga batun sulhu ta dawo karbar kudi.
Kai-tsaye : Yaushe ne za’a cigaba da sauraran shari’ar Ganduje da Abba?
Kotun daukaka kara ta sanya ranar shari’ar Ganduje da Abba
Kotu a Kano ta yankewa mai cin zarafin kananan yara hukunci
Haka shima wanda ake bi bashin Malam Bashir Fari Sharada ya bayyana cewa ,daga wannan ranar da kotun ta sulhuntasu bata kara neman sa ba, amma hakan alkali yayi hukuncin zuwa asayar da gidan sa ba tare da sanin sa ba.
Ya sake bayyana cewa, yana zauna ne da iyalin sa suna karin kumallo kwatsam sai sukaji an sako kai cikin gidan ana fatali da kayansu.
Akan haka ne Malam Bashir Fari Sharada ya bayyana bakin cikinsa duba da cewa wadanda aka je da su gidan shi har da Kurame domin ba za su iya jin irin roko da magiyar da yake musu ba,
Ya kara da cewar irin tozarcin da su kai masa har ma takai da iyalisa su kwana a makwabta shi kuma ya kwana a shagon damin acewar sa maganar siyar da gidan sa ta tabbata.
Hakan yasa ya daukaka kara shida lauyansa domin dakatar da Alkalin Sharif daukar matakin yanke hukuncin a baya, amma hakan bai samu ba saboda an dauke alkalin kotun wanda ya yanke hukuncin farko.
Amma kakakin babbar kotun jihar Kano Baba jibo Ibrahim ya ce alkalin babbar kotun jiha ya mayar da martanin cewa har idan wannan korafi yaje waje sa sai abin da ya tubewa buzu nadi.
Labarai
Wani dan kasuwa ya gamu da ajalinsa sakamakon harbin bindiga

Dan sandan dai yana gadi ne a wani Banki yayin da ya hango wannan mai mota ya buge wani mutum kuma wasu ‘yan sanda dake aiki a bakin titi suka bukaci shi daya bude motarsa a saka wanda yaji raunin amma kuma yaki bayan da aka yi zargin cewar yana son ya tsere.
Amma sai yaki bin umarnin su hakan ya sanya dan sanda dake zaune yana aikin gadi ya ja kunamar bindigarsa ya harbi wannan matukin motar kuma nan take ya rasu.
Rundunar ‘yan sanda ta Kano ta yi holin masu yin garkuwa da mutane
Kano: Lauyoyi sun yi barazanar gurfanar da kwamishinan ‘yan sanda
Jihar Kano ta sami sabon kwamishinan ‘yan sanda
Hakan tasa abokin tafiyar direban ya kasa magana saboda dimaucewa da yayi ganin abinda yafaru da wanda suke tare.
Tuni dai tawagar ‘yan sanda suka halacci gurin da abin yafaru karkashin jagorancin babban mukaddashin kwamishinan’ yan sanda na Kano mai lura da ayyukan yau da kullum DSP Balarabe sule.
Kakakin rundunar ‘yan sanda ta jihar DSP Abdullahi Haruna ya ce rundunar na tattara bayanai kafin gurfanar da wanda ake zargi a kotu
Labarai
Hukumar Hisbah ta ziyarci makarantar ‘yan mari ta zamani

Babban kwamandan hukumar ta jihar Kano Sheik Harun Muhad Sani Ibn Sina da kuma baban daraktan hukumar Dr, Aliyu Musa Kibiya sun kai ziyarar aiki makarantar ‘yan Mari ta zamani dake karamar hukumar Kura anan jihar Kano wanda Asusun tallafawa na Annur ya kafa.
Makarantar ‘yan Marin ta zamani wanda Dr, Aliyu Musa Kibiya ya asasa da nufin karfafa samar da ingantaccen ilimi mussaman ma na Al-qur’ani mai girma don taimakawa a kokarin da gwamnati ke yi na ganin ana bada ilimin Al-qur’ani ta hanyar data dace a jihar Kano.
Haka zalika Tsangayar ko makarantar ‘Yan marin irin ta ce ta farko a jihar Kano da aka taba kafawa ta zamani.
Wannan na kunshe cikin sanarwar da jami’in yada labarai na hukumar ta Hisbah Lawal Ibrahim Fagge \ya sanya hannu cewa, tsangayar na da ajujuwa guda 27 da dakunan kwana na dalibai 35 da masallaci.
Hisbah na shirin kara inganta ayyukanta a kananan hukumomi
Laifin iyaye ne ke haifar da mace-macen aure -Hisbah
Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta lalata kwalaben barasa 196,400
Ana dai kyautata zaton cewar a kwanan ne gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje zai kaddamar da Tsangayar ta zamani a cikin wannan shekarar yayin da kuma za’a koma karatu gadan-gadan nan bada jimawa ba.
-
Labaran Kano6 months ago
Sarki Muhammadu Sunusi II ya amsa takardar tuhumar da gwamnatin Kano ke masa
-
KannyWood2 months ago
An fara sulhu tsakanin jaruman da suka yi auren mutu’a
-
KannyWood2 months ago
Abinda yasa ‘yansanda suka cafke Sadiya Haruna
-
KannyWood2 months ago
Abinda ya sanya ba zan iya auren Yawale a zahiri ba -Rayya
-
KannyWood2 months ago
Yadda akayi auren mutu’a a Kannywood
-
Labarai2 months ago
An garkame Sadiya Haruna a gidan yari
-
KannyWood2 months ago
Kun san abinda ya hana jaruma Maryam Yahya aure?
-
Manyan Labarai2 months ago
An gano wanda ya fito a bidiyon da ake zargin Daurawa ne