Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ko mene ne makomar ‘yan marin da ake sakowa?

Published

on

‘Yan mari sun shaki iskar ‘yanci a Kano

A ‘yan kwanakin nan ne, mahukunta ke ta sako matasan da ke daure cikin mari a gidajen gyaran tarbiyya da ke sassan jihohin Najeriya.

Sai dai yanzu haka kallo na shirin komawa kan makomar wadanda aka sako din na cewar ko ya ya ake ganin sakin nasu bayan sun dawo cikin al’umma, kasancewar tun da fari an killace su ne sakamakon wasu laifuka da suke aikatawa.

A dai ‘yan kwanakin da suka gabata ne jami’an ‘yan sanda suka samu nasarar kubutar da wasu da ke gidan marin a jihohin Kaduna da garin Daura na jihar Katsina.

Haka ma a nan Kano inda aka ruwaito cewa, wata makaranta ta ‘yan mari ta saki mutane 100 bisa radin kanta, inda wasu ke cewa hakan na da alaka da yadda ‘yan sanda suka rika kubutar da tsararrun.

Masana da dama dai na cewa, kamata ya yi a yi kokarin tsaftace harkar tafiyar da gidajen gyaran tarbiyyar maimakon rika sako ‘yan marin suna fantsama cikin jama’a.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!