Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ganduje ya hana iyayen yara Magana da yan jarida

Published

on

Kano state Governor Abdullahi Umar Ganduje

Gwamna Abdullahi Ganduje ya ja hankalin iyayen da aka ceto ‘yayansu daga Onitsa jihar Anambra da su yi hankali da yan jarida kungiyoyi masu zaman kansu.

Gwmamna Ganduje ya bayyana haka ne ayayin da rundunar yan sanda jihar Kano ke mika wadannan yara hannun gwamnati a ranar litinin da ta gabata.

Wannan dai na kunshe ne cikin wata sanarwar mai dauke da sa hannun daraktan yada labarai na gidan gwamnati Aminu Yassar ya fitar kamar yadda jaridar Kano Focus ta rawaito.

Gwamna Ganduje ya ja hankalin iyayen yara da yaran da su kauracewa zantawa da yan jarida da kungiyoyi masu zaman kansu, gudun kada wasu yan jaridun ko kungiyoyi masu zaman kansu samun damar amfani da su domin cimma wata manufa ta su.

An yiwa daya daga yaran Kano da aka sace fyade

Yana mai jaddada cewa hukumomin tsaro na gudanar da bincikensu gudun kada hakan ya kawo cikas ga bincikensu.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!