Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An dambata tsakanin KAROTA da Sojoji

Published

on

Da tsakar ranar yau ne wata hatsaniya ta barke tsakanin wasu jami’an sojoji da na ‘yan KAROTA a kan kwanar kasuwar Sharada inda kuma aka baiwa hammata iska.

Rahotanni dai sun bayyana cewa rikicin dai ya samo asali ne sakamakon aron hannu da ake zargin Sojojin sun yi don raste hanya, duk kuwa da cewa ba hannunsu bane, wanda kuma hakan ya sabawa doka, dalilin kenan da ya sanya ‘yan KAROTAR suka tare su.

Wasu shaidun gani da ido sun bayyana mana cewa ana tsaka da musayar yawu ne wani daga cikin sojojin ya doki dan karotar a ka har ya fasa masa kai.

Ko da muka tuntubi hukumar KAROTA don jin ko me hukumar za ta ce, jami’in hulda da jama’a na hukumar Nabulisi Abubakar Kofar Na’isa ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce yanzu haka ma maganar tana hannun ‘yan sanda.

An gurfanar da shugaban KAROTA a gaban Kotu

Hukumar KAROTA zata ware jami’an da zasu kula da cinkoson Safiya da dare

Jami’an KAROTA sun jikkata wasu matasa

Kakakin rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano DSP Adullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar da afkuwar al’amarin ga tashar Freedom Redio ya ce jami’in sojan yana hannun su yayin da kuma suke neman Mai Adai-Adaita sahun bayan ya da ya cika wandan sa da Iska

Wakilinmu Umar Lawan Tofa ya rawaito cewa rikicin ya fara ne daga Kwanar Kasuwar Sharada har ta kai zuwa kan titin Yahaya Gusau.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!