Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za’a daina dogaro akan Tumatirin kasashen waje

Published

on

Kungiyar manoman Tumatir ta kasa ta ce nan ba da dadewa ba, kasar nan za ta daina dogara da Tumatirin da ake shigo da shi daga kasashen waje.

Shugaban kungiyar reshen jihar Kano Alhaji Sani Dalladi Yadakwari ne ya bayyana haka, yayin bikin rabon iri na zamani da aka rabawa manoman tumatir, a garin kadawa da ke yankin karamar hukumar Garun Malam a nan jihar Kano.

Ya ce, bikin rabon irin tumatirin da aka guidanar a yau, zai taimaka gaya wajen bunkasa noman tumatiri a jihar Kano.

Da ya ke nasa jawabin, Shugaban kamfanin tumatirin da ya yi rainon irin, Alhaji Abdulkadir Kaita, cewa ya yi, manoma dubu goma ne za su fara amfana ta cikin shirin a zangon farko.

Dangote: ya kafa kamfanin rainon irin timatiri a Kano

Wasu daga cikin manoman Tumatirin da suka amfana ta cikin shirin sun ce, za su yi amfani da irin da aka basu wajen bunkasa noman da su ke yi.

Wakilin mu Shamsu Da’u Abdullahi ya ruwaito cewa, rabon irin wanda daya ne daga cikin shirin tallafawa manoma na Ancho Borrowers da babban bankin kasa CBN ke gudanarwa, ana saran manoman tumatir dubu dari ne za su amfana nan da shekara daya.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!