Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Maza sunfi bada muhimmanci ga sunnar karin aure –Halima Shitu

Published

on

Tsohuwar mataimakiyar babban kwamandan Hisbah na jihar Kano, kuma shugabar kungiyar mata musulmi ta Africa wato (AMWA) Malama Halima Shitu Abdulwahab ta bayyana cewa babu wata Sunnah da maza sukafi baiwa muhimmanci face sunnar kara Aure.

Malamar tayi wannan jawabi ne a yayin taron da mai dakin Sarkin Kano Hajiya Maryam Muhammad Sanusi II ta shirya a fadar sarki wanda aka yi a you don dakile rikicin cikin gida tsakanin iyali a Arewancin kasar nan.

Malam Halima shitu ta kara da cewa mace tana da daraja tana da kimar da har Allah madaukakin sarki ya yi mata, a saboda haka ya sanyawa sura guda sunan Maace wato Suratul Nisa’i.

Har ila yau malamar ta Kara da cewar, da za’a tara mata ‘yan uwa to tabbas zata yi musu wa’azi akan irin hakkokin da Allah ya dora musu na matayen su, sai dai abun takaicin shi ne basa maida hankali akan su, illa kawai kan batun karin Aure.
Wakiliyar mu Samira Sa’ad Zakirai ta rawaito cewa malamar na ambato muhimman batutuwa da ya kamata namiji ya yi wajen sauke nauyin da rataya a wuyan sa da suka hada da nemowa matarsa abinci da sha da kuma sutura ya kuma bata cikakkiyar kulawa, wannan itace cikakkiyar sunnar manzon Allah SAW.

Rubutu masu alaka:

Tilas a magance cin zarafin mata- Mai dakin Sarkin Kano.

Za’a koyar da fursunoni arba’in karatun Firamare

Kano na da daliban sakandire fiye da dubu dari bakwai  (700,000)

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!