Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Rundunar ‘yan sandar jihar Kano ta sake ceto wani yaro a Anambra

Published

on

Rundunar ‘yan sandar jihar Kano ta ceto wani yaro dan shekara 11 da aka sace daga unguwar PRP  da ke unguwar brigade a nan Kano, a shekara ta 2014 aka kuma sayar da shi a jihar Anambra.

Kakakin rundunar ta ‘yan sanda DSP Abdullahi Haruna ya ce  Paul Onwe da Mercy Paul ne suka  sace tare da sayar da yaron  mai suna Muhammad Ya’u, a kan kudi naira dubu dari biyu.

Ya kara da cewa  tuni aka mayar da Muhammad Ya’u addinin Krista aka kuma canza masa suna Chinedu Ogbodo daga hannun wadanda suka saye shi.

Rahotannai na nuni da cewar tuni aka kama wadanda ake zargin da sace yaro su uku, inda kuma yanzu haka suke karkashin binciken ‘yan sandabinciken ‘yan sanda , biyo bayan yara tara da aka ceto a yan kwanakin nan.

DSP Haruna ya ce rundunar na iya kokarinta wajen ceto yara yan Kano da aka sace tare da sayar da su a jihar ta Anambra

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!