Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kano9: Har yanzu akwai yara sama da 90 da ba’a gano ba -inji iyayen yaran

Published

on

Kungiyar iyayen yara da aka sacewa yara ta jihar Kano ta ce har yanzu akwai sama da yara casa’in da daya da masu satar yara suka sace a wasu daga cikin unguwannin jihar Kano.

Shugaban kungiyar na jihar Kano Isma’il Ibrahim Muhammad ne ya bayyana hakan a yau lokacin gudanar da addu’oi’n neman taimakon Allah ya bayyana musu sauran ‘ya’yansu da masu satar yara suka sace a jihar Kano.

Ismail Ibrahim ya kara da cewa cikin unguwannin da satar kananan yaran tafi kamari akwai unguwar Hotoro, Kawo, Yankaba da sauran unguwanni, a don hakane suke kira ga gwamnati da ta kara kaimi wajen an gano musu sauran ‘ya’yansu da aka sace.

Wakilin mu Abdulkarim Muhammad Abdulkarim Tukuntawa ya rawaito cewa manyan malamai da dama ne suka halarci taron addu’ar da iyayen yaran da aka sace da kuma sauran al’ummar gari.

Labarai masu alaka:

Kano9: Karanta cikakken labarin yaran Kano da aka sace

Kano9: Al’umma suna ta karrama kwamishinan ‘yan sanda sakamakon ceto yaran Kano

Kano10- An sake ceto wani yaro daga jihar Anambra

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!