Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kano10- An sake ceto wani yaro daga jihar Anambra

Published

on

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano ta sake gano  wani Yaro tare da ceto shi daga jihar Anambra wanda wasu suka sace shi  mai suna Salisu.

Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Kano Ahmad Iliyasu kuma mataimakin babban sufeton ‘yan sanda na jihar Kano ya bayyana hakan taron manema labarai a jiya Alhamis.

Hakazalika Kwamishina Ahmad Iliyasu ya ce a halin yanzu ba yara tara ba ne yara goma ake magana.

Ahmad Iliyasu ya ce a jiya yaron Salisu suna kan hanyar su ta zuwa a nan Kano amma kuma ana kyautata zaton cewar za su iso yau da safe.

An mika yaran da aka sace ga iyayen su a Gombe

Kano9: Al’umma suna ta karrama kwamishinan ‘yan sanda sakamakon ceto yaran Kano

‘Yan sanda sun kara ceto yara biyu da aka sace a Anambra

Idan za’a iya tunawa a kwanakin baya ne rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano ta sanar da cewar ta ceto yara tara 9 ‘yan asalin jihar Kano da aka sace su aka kuma saida su a can jihar Anambra.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!