Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Gwamnatin tarayya za ta samar da wuta mai amfani da hasken rana

Published

on

Ministan wutar lantarki na kasa Injiniya Sale Mamman, ya ce akwai bukatar samar da karin manyan dama -damai da za su kara inganta harkar samar da wutar lantarki a kasar nan.

Injiniya Sale Mamman na bayyana hakan ne yayin zantawar sa da gidan radiyo freedom kan cika shekaru dari da yayi a ofis na irin ayyukan da ya gabatar a ma’aikatar.

Ya ce ana sa ran samun wutar lantarki mega watt dari bakwai a tafkin Shiroro da na kainji, wanda a yanzu da kyar ake iya samar da mega watt dari hudu, hakan na daya daga cikin kalubalen da ke kawo koma baya a sha’anin wutar lantarki a kasar nan.

Ya kuma ce ma’aikatar wutar lantarki sun dukufa wajen ganin ta ci gaba da samar da wutar lantarki yadda ya kamata musamman ta hanyar hasken rana da iska.

Sale Mamman ya kuma ce duba da rashin ishashiyar wutar lantarki da ake samu a Arewacin kasar nan ne ya sanya ma’aikatar za ta samar da Karin tashohin wutar a nan Arewa musamman a jihar Kano dan inganta masana’antun dake yankunan.

Injiniya Sale Mamman ayayin tattaunawar ya kuma ce, manyan kamfanonin dake karbar wutar dan rabawa ga al’umma suna daya daga cikin wadanda ke kara ta’azzara rashin wuta a kasar nan ta yadda idan an turo wutar basa iya karba dan rabata ga jama’a.

Ya kuma ce kamfanonin dake raba wutar a kasar nan sunfi so sukai ta zuwa unguwannin da suke biyan su kudade masu Asoka ko kuma kamfanoni, ta yadda ta hakan ne kadai suke iya samun kudade masu yawa.

Injiniyya Sale Mamman ya ce jihohi da dama a kasar nan da dama basa iya biyan kudin wutar da suka karba, inda ya buga misali da jihar Lagos da cewa bata iya biyan kashi daya cikin hudu na kudin wutar da ake bata a duk wata.

Shugaban ya ce hanya da ya ce za’a iya bi dan magance matsalar rashin samun ishashiyar wutar lantarki ,ita ce samar da mitoci a gidaje ta yadda kowa zai iya sanin wutar da yake sha, suma masu kamfanonin su samu saukin karbar kudaden wutar a hannun al’umma.

Inda ya ce ma’aikatar ta na nan ta na gudanar da tsari ta yadda za ta sanyawa kowanne gida da shaguna da kamfanoni mita yadda kowa zai dinga sanin wutar da yake sha kuma za’a sanya mitocin ba ko sisin mutun ta yadda za’a dinga cire kudin mitar ahankali har mutun ya gama biya.

Ya ce yanzu ma’aikatar na nan na duba yiwuwar samun masalaha tsakanin masu karbar wuta da masu rabata yadda za’a samu ingantacciyar wuta musamman yadda za’a cigaba da samun cigaban tattalin arzikin da ya kamata.

Injiniyya Sale Mamman ya ce ma’aikatar na nan na kokarin shigo da tsarin da zai baiwa kananan ‘yan kasuwa wutar lantarki suna sayar da ita ga al’umma ta yadda wadanda ke bukatar wutar da yawa za su dinga samunta yadda ya kamata dan saukaka musu aiyuukan su da cigaban tattalin arzikin su.

Ko da aka tambaya shi wasu kasashen da ke makwabtan da kasar nan ke samun wuta awanni ashirin da hudu batare da daukewa ba kuma suna samun wutar ne daga nan Najeriya sai ya ce kasashen na biyan kasar nan kudin wuta yadda ya kamata sabanin yadda abin yake a nan gida Najeriya.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!