Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Manyan Labarai

Mun warware korafe-korafe masu dinbim yawa- Muhyi Magaji

Published

on

Shugaban hukumar karbar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano, Barista Muhyi Magaji Rimin Gado ya bayyana cewa hukumar ta karbi dinbim korafe-korafen al’ummar jihar Kano, da ta samar musu mafita a shekarar da ta gabata.

Barista Muhyi Magaji Rimin Gado ya bayyana hakan ne yayin tattaunawa da manema labarai, a sakatariyyar ‘yan jaridu dake nan Kano.

Ya ce shakka babu hukumar tayi amfani da tanade-tanaden doka wajen gurfanar da wadanda ake zargi da laifukan cin hanci da rashawa a sassan jihar Kano daban-dabam.

Barista Muhyi Magaji Rimin Gado ya kuma bukaci al’ummar garin Kano da su rungumi dabi’ar amfani da guraben da gwamnatin Kano ta ware don saka koken su kan abubuwan da suke faruwa ba dai-dai ba a jihar don daukar matakin gyara.

Wakilin mu Umar Idris Shuaibu ya ruwaito hukumar karbar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano na kira wajen neman goyon bayan al’ummar jihar Kano, tare da basu cikakkun bayanai don gudanar da ayyukan su.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!