Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Wasu mata biyar sun rasa rayukan su a Kano

Published

on

A jiya Alhamis ne wasu mata su biyar suka rasa rayukansu  yayin  yaro guda kuma ya jikkata lokacin da suke tsaka da debar kasa cikin waani ramin tono a kauyen Dauni cikin karamar hukumar Minjibir.

Shaidun gani da a kauyen sun ce matan na tsaka da tono kasar ne a cikin ramin sai kasa ta rubta musu tare da binne su a ciki.

Mazauna kauyen sun bayyanawa Freedom Rediyo cewa matan kauyen dama sun dade suna tono wannan kasa daga ramin suna kawowa kasuwar Kofar-Wambai a babban birnin jiha suna sayarwa.

Shaidun sun kara da cewa tuni dai aka yi jana ‘iza tare da binne mata biyar din da suka rasu a kauyen.

Kazalika  shi kuma yaron da suka ce dan kimanin shekaru biyar ne da aka zakulo da ransa ya samu raunuka, sai dai ba ‘a bayyana ko an kai shi asibiti ba ko a’a.

Rashin kwararrun masu karbar haihuwa ke janyo mutuwar jarirai- Likita

Ana zargin likita da sanadin mutuwar mara lafiya

An zargi jami’an SARS da  sanadiyyar mutuwar wani matashi

Mazauna kauyen dai ba su fadi takamaiman abinda ake yvi da kasar da matan ke kaiwa kasuwar Kofar-Wamban suna sayarwa ba, sai dai wasu sun ce ana amfani da ita ne wajen hada hodar kwalliyar mata.

Jamiin yada labarai na karamar hukumar Minjibir,  Tasi’u Dadin Duniya da kuma takwaransa na hukumar kashe gobara ta jihar Kano, Saidu Mohammed Ibrahim sun tabbatar da afkuwar lamarin amma ba su yi karin bayani ba.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!