Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnati ta dakatar da wasu daliban Sakandire a Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta dakatar da wasu daliban makarantar sakandiren kimiyya da fasaha ta garin Dawakin Tofa, sakamakon tarzoma da suka gudanar a daren jiya Juma’a.

Shugaban hukumar kula da makarantun kimiyya da fasaha ta jihar Kano, Alhaji Ahmad Tijjani Abdullahi ne ya bayyana haka, yayin wata ziyara da ya kai makarantar a yau asabar.

Ya ce, sun dauki wannan matakin tura yaran ga iyayen su ne, domin basu damar gudanar da binciken kwa-kwaf kan dalilin faruwar lamarin.

Sai dai, ya ce, an tura daliban gida na tsawon mako daya ne kacal kafin a kammala binciken.

Karin labarai:

Daliban Sakandire sun yi zanga-zanga a Bauchi

An rufe wata makarantar sakandire a Kaduna

Rahotanni sun ce, a daren jiya juma’a ne wata rigima ta barke tsakanin shugabannin daliban makarantar da sauran dalibai, wanda sanadiyar haka aka lalata kadarori da dama a makarantar.

Bayanai sun ce, daliban wadanda suke a shekarar karshe sun kori shugabanninsu wadanda suka tsere zuwa cikin gari tare da kone kayayyakin su.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!