Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

A dinga tallafawa masu bukata ta musamman – Kungiya

Published

on

Wata kungiya mai zaman kanta dake aiki a jihar Niger ta tallafawa masu bukata ta musamman da tallafin kudi dai-dai lokacin da ake fuskantar matsalolin tattalin arziki.

Shugabar kungiyar Dorothy Nuhu ta bayyana hakan ne a karshen makon da ya gabata, yayin wani taron wayar da kan jama’a masu bukata ta musamman kan annobar COVID-19.

Kungiyar dai ta raba musu kudi da kayayyakin abinci a birnin Minna, a wani mataki na rage musu radadin matsalolin tattalin arziki da aka fuskanta a dalilin COVID-19.

Dorothy Nuhu ta kara da cewa, wanda suka ci gajiyar tallafin sun fara ne daga shekaru 10 zuwa 19 a yankunan Chanchaga da Bosso da kuma Shiroro.

Shugabar na cewa, kowannen su ya samu Naira dubu ashirin da biyar da buhun shinkafa da da dai sauran kayan masarufi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!