Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

A riƙa tausayawa talakawa –Sarkin Kano ga mahukuntan Asibitin Dala

Published

on

Mai martaba sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya buƙaci mahukuntan asibitin ƙashi na Dala, da su samar da tsarin ragewa marasa lafiya raɗaɗin kuɗin magani da kuma inganta ayyukan kula da su.

Sarkin yayi wannan kira ne lokacin da ma’aikatan asibitin ƙashi na Dala ƙarƙashin jagorancin sabon shugaban asibitin Dakta Nuraddeen iIsah suka ziyarce shi a fadar sa.

Alhaji Aminu Ado Bayero ya ce, akwai buƙatar hukumomin asibitin su yi la’akari da halin matsin rayuwa da aka shiga a wannan lokaci, don sauƙaƙawa al’umma.

A nasa jawabin Sabon shugaban asibitin Dakta Nuraddeen Isah, ya tarbatarwa da sarkin cewa, za su samar da sabon tsarin don ganin an taimakawa marasa lafiya, ciki har da samar da motoci don ɗauko marasa lafiya.

Wakilinmu na masarautar Kano Shamsu Da’u Abdullahi ya rawaito cewa, yayin ziyarar Dakta Nuraddeen Isah ya ce, sun horar da likitoci daban-daban domin kula da lafiyar al’umma da kuma magance fita ƙasashen ƙetare don neman lafiya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!