Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Abduljabbar na fama da rashin lafiya a gidan gyaran hali

Published

on

Lauyan Malam Abduljabbar Kabara Barista Rabiu Shu’aibu Abdullahi ya tabbatar da cewa malamin bashi da lafiya yanzu haka da yake tsare a gidan gyaran hali.

Sai dai Barista Rabiu ya musanta zargin da ake yaɗawa cewar an sakawa malamin guba a abinci a gidan gyaran halin da yake tsare.

“tabbas Malam bashi da lafiya, amma tuni an samo likita ya duba shi kuma ya bashi magani, har ma ya samu sauki a halin yanzu” Lauyan Abduljabbar.

Itama hukumar kula da gidan gyaran hali na Kano DSC Musbahu Lawan Kofar Nasarawa ya ce, malamin bai taba shan ruwa ko abincin gidan gyaran hali ba, a don haka babu wani abu da ya same shi.

“Mun samu labarin wani lauya ne ya fitar da labarin cewa an ba shi guba a inda ya ke tsare, wannan ne ya sanya muka baza jami’an mu don gano wanda yayi wannan kalami tare da ɗaukar mataki a kan sa” inji DSC Musbahu Lawan Kofar Nasarawa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!