Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Mutane 60 ne suka mutu sanadiyyar cutar Amai da Gudawa a Abuja – FCTA

Published

on

Gwamnatin Babban Birnin Tarayya Abuja na cigaba da wayar da kan al’umma game da barkewar cutar amai da gudawa da tayi kamari a yanzu.

Ministar Babban Birnin Tarayyar, Dakta Ramatu Aliyu ce ta bayyana haka yayin gangamin wayar da kan al’umma game da cutar a yankin Pyakasa da Gwagwa dake Abuja.

Kawo yanzu, adadin wadanda suka mutu sakamakon cutar ya karu daga 54 zuwa 60.

Haka zalika, wadanda ake zaton sun kamu da cutar a yankin sun tashi daga 604 zuwa 698 cikin kwanaki 3.

Ministar ta bukaci mazauna birnin na FCT da masu ruwa da tsaki da su sanar da hanyoyin da al’umma za su bi wajen yin rigakafin cutar da tsaftace muhalli tare da kiyaye tsabtar hannuwa a koda yaushe.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!