Labarai
Abinda da ake yadawa a kaina kan makomata a siyasa karya ne- Kwankwaso

Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya yi watsi da rahotanni da ke alaƙanta cewa yana daf da komawa wata jam’iyya, da kuma batun cewa zai shiga haɗaka da wasu jam’iyyu, lamarin da ya ce ƙanzon kurege ne kawai domin ba da yawunsa ba.
Wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X, Kwankwaso ya ce raɗe-raɗin baida tushe balle makama kuma labaran ƙarya ne kawai na siyasa.
Ya ce, ya daina yin tsokaci kan lamuran siyasa da ke faruwa a Najeriya, kuma zai ci gaba da yin haka har zuwa wani lokaci.
Don haka ne, ya buƙaci al’umma da su amince da sakonni da suka fito daga shafukansa da kuma majiyoyi da aka yarda da sahihancinsu ba daga wasu wurare na daban ba.
You must be logged in to post a comment Login