Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Siyasa

Haryanzu Kwankwaso na nan a PDP-Bashir Sanata

Published

on

Sakataren yada labaran jami’iyyar PDP a nan Kano Bashir Sanata ya musanta labaran da ke cewa tsohon gwamnan Kano Sanata Rabiu Musa Kwankwaso na shirin ficewa daga jami’iyyar.

Bashir Sanata ya bayyana haka ne a zantawarsa da Freedom Radio.

Ya ce, labarin da wasu jaridu a kasar nan ke ci gaba da ya dawa sam babu kanshin gaskiya a ciki, domin kuwa lokaci ne kawai zai fayyace ko Kwankwason zai ci gaba da zama a PDP ko kuma zai fice daga jami’iyyar.

“Zan iya cewa wasu jaridu ne da suke so a ce sune suka fara yada labarin, wanda kuma babu kanshin gaskiya a ciki ko kadan,” a inji Bashir Sanata.

Wannan dai na zuwa ne a dai dai lokacin da rahotanni ke bayyana Sanata Kwankwaso na shirin ficewa daga jami’iyyar PDP zuwa jami’iyyar NNPP a kasar nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!