Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

ACF:ta bukaci Atiku Abubakar da amince da sakamakon zaben shugaban kasa

Published

on

Kungiyar dattawan Arewa ta ACF ta bukaci dan takaran shugaban kasa karkashin jam’iyyar PDP Atiku Abubakar da ya amince da sakamakon zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar ashirin da uku ga watan Fabrairu.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren yada labaran kungiyar Muhammed Ibrahim Biu.

Sanarwa da aka fitar da ita jiya a Kaduna, ta bukaci tsohon mataimakin shugaban kasar da ya amince da zabin jama’a.

Kungiyar ta ACF ta cikin sanarwar dai ta kuma yabawa jajircewar Atiku da kuma kokarin da ya yi a yayin zaben, a don haka ta ce amincewa da sakamakon zai kara mishi mutunci a idon jama’a. Sanarwar ta kungiyar ACF ta ma buga misali da cewa ganin cewa an gudanar da zaben cikin lumana ba tare da samun tashin hankali masu yawa ba kuma kungiyoyin sanya idanu sun yaba da nagartar sakamakon, a don haka zai fi kyautatuwa Atiku Abubakar ya amince da sakamakon

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!