Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Alkalan da suka yi shari’a kuskure suka yi: Abba Kabir

Published

on

Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ce alƙalan kotun da ta gudanar da shari’ar zaɓen gwamnan jihar sun yi kuskure a hukuncin da suka yi na soke zaɓensa.

A ranar Laraba 20 ga watan nan na Satumba ne kotun wadda ta saurari ƙarar da jam’iyyar APC ta shigar tana kalubalantar nasarar da hukumar zaɓen Najeriya INEC ta bai wa Abba Kabir Yusuf a matsayin gwamnan jihar a zaɓen da aka yi ranar 18 ga watan Maris na 2023 ta soke nasarar.

Kotun wadda ta gabatar da hukuncinta ta manhajar Zoom ta ce tsohon mataimakin gwamnan jihar, Nasir Yusuf Gawuna na jam’iyyar APC ne ya ci zaɓen.

Ta ce ta soke ƙuri’a 165,633 da ta ce aringizo ne aka yi wa ɗan takarar jam’iyyar NNPP, wanda tun farko hukumar zaɓe ta ce ya samu ƙuri’a 1,019, 602.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!