Labarai
Ambaliyar ruwa na ci gaba da mamayar jihar Bauchi
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2021/08/WhatsApp-Image-2021-08-23-at-7.29.00-AM.jpeg)
Maimartaba Sarkin Bauchi Dr. Lirawanu Sulaiman Adamu ya yi kira ga masu hannu da shuni da su tallafawa waɗanda ambaliyar ruwa ta shafa a jihar.
Sarkin ya bayyana hakan ne, yayin da ya ziyarci sansanin waɗanda ambaliyar ruwa ta raba da gidajen su.
Hukumomi a jihar, sun tabbatar da rasuwar mutane 8 sanadiyyar ambaliyar tare da asarar dukiya ta sama da miliyan ɗari biyu.
Ambaliyar dai ta fi ƙamari a wasu yankunan na ƙaramar hukumar Kirfi.
You must be logged in to post a comment Login