Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ambaliyar ruwa yayi sanadiyar tashin manoma daga gonakinsu a Adamawa

Published

on

Manoma a karamar hukumar Ganye dake a Jihar Adamawa sun koka dangane da yadda ambaliyar ruwan Daya sakko daga dutse, ya Kuma taho da yashi ya rufe musu gonakinsu.

Daya daga cikin manoman da wannan matsalar ta shafar ya shaidawa freedom Radio cewa ‘ambaliyar ruwan ta shafi gonakin ba addadi, Wanda zai iya haifarda koma baya a bangaren noma a yankin, dama wasu bangarorin kasar nan’.

Manomin ya ce ‘ko a gonarsa kadai Yana iya noman wake buhu goma, na masara goma, sai dai kuma bayan wannan matsalar ta auku bashi da damar yin hakan’.
A don haka manoman suka bayyana cewa idan har ba’a samarwa ruwan tsayayyiyar hanyar wucewa daga kan Dutsen zuwa kogi ba, to shakka babu basu da masaniya Kan irin matsalar da zasu tsinci kansu a nan gaba, duba da cewa har yanzu a cikin damunar ake.

Rahoton: Nuraddin Usman Ganye

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!