Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Sarki Aminu Ado Bayero ya umarci shugabannin POLAC su rika daukar dalibai masu kwazo

Published

on

Mai martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero, ya umarci shuwagabanin makarantar horas da yanda sanda da ke garin Wudil da su rika daukar dalibai masu hazaka domin ingantawa tare da tabbatar da tsaro a fadin Nijeriya.

Sarkin ya furta hakan ne lokacin da ya karbi ba kuncin shugabanin gudanarwar makarantar bisa jagorancin sabon Kwamandan makarantar AIG Sadik Abubakar a fadarsa.

Alhaji Aminu Ado Bayero, ya ce, aikin ‘yan sanda na da matukar mahimmanci duba da yadda ake samun bata gari suna lalata dukiyoyin al’umma.

A nasa jawabin sabon Kwamandan makarantar AIG Sadik Abubakar, ya ce, sun kai ziyara fadar sarkin ne domin yi masa gaisuwar ban-girma tare da gabatar da kansa amatsayin sabon kwamandan makarantar.

Rahoton: Shamsu Da’u Abdullahi

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!