Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An bude Sabon Masallaci a Rangaza Inkyan

Published

on

An bude sabon Masallacin Kamsussalawati, a unguwar Rangaza Inkyan dake Layin Mai Garin Rangaza a Karamar hukumar Ungogo.

Masallacin wanda wani matashi kuma dan Kasuwa, Alhaji Salisu Yahaya Bagobiri, ya Gina, an samar dashi ne ga Al’ummar yankin don cigaba da gudanar da Ibada.

Da yake jawabi, ga Freedom Radio, jim kadan bayan kaddamar da Masallacin, daya daga cikin Jagororin matasan yankin, Mustapha Abdullahi Kwamred, ya bukaci Attajirai da masu hali a cikin Al’umma dasu cigaba da tallafawa jama’a ta hanyoyin daban-daban, musamman wajen yin Sadakatul Jariya ta hanyar ciyarwa ko hidimtawa Addini.

“Matashin ya saka Danba, ga Al’umma musamman ma masu Hannu da Shuni, kasancewar ba Hidimtawa Addini kadai ya tsaya ba, har ma da taimakawa Marayu da Marasa Galihu,” inji Mustapha Abdullahi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!