Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An gurfanar da Buhari gaban kotu kan ciyo bashi

Published

on

Kungiyar tabbatar da gaskiya da daidaito a ayyukan gwamnati (SERAP) ta gurafanar da shugaban kasa Muhammadu Buhari gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja, tana bukatar kotun ta haramta musu ciyo bashi daga asusun ‘yan Nigeria da suka jima ba su yi amfani da shi ba.

Kudaden da gwamnati ke son ciyo bashinsu daga asusun ajiyar banki na ‘yan kasa wadanda suka jima ba su yi amfani da su ba, sun kai naira biliyan dari takwas da miliyan casa’in da biyar.

Cikin takardar karar mai lamba FHC karan-tsaye ABJ karan-tsaye CS karan-tsaye 31 karan-tsare 2021, mai kuma dauke da sa hannun lauyoyin kungiyar ta SERAP Kolawale Oluwadare da Adelanke Aremo ta bukaci kotun da ta haramta daukar wannan mataki da gwamnati shugaba Buhari ke shirin yi.

Kungiyar ta SERAP ta ce taba kudaden ya sabawa doka, a don haka ta ce, ba daidai bane gwamnatin tarayya ta ciyo bashi daga cikin asusun ajiya na jama’a ba tare da amincewar su ba.

Sauran wadanda kungiyar ta SERAP ta sanya cikin wadanda ta ke kara akwai: gwamnatin tarayya, da attorney janar na kasa kuma ministan shari’a Abubakar Malami, shugaban majalisar dattijai Sanata Ahmed Lawan, da takwaransa na wakilai Femi Gbajabiamila da kuma ministar kudi, kasafi da tsare-tsare Zainab Ahmed.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!