Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

NFF: Ta musunta zaben Amaju Pinnick a matsayin mataimaki na 5 ga shugaban CAF

Published

on

Hukumar kwallon kafa ta Najeriya NFF ta musunta jita-jitar da ke cewa an zabi shugaban hukumar Amaju Pinnick a matsayin mataimakin shugaban hukumar kwallon kafa ta Afirka CAF na biyar da aka gudanar a birnin Rabat da ke kasar Morocco.

Hakan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da babban sakataren hukumar ta NFF Dakta Mohammed Sanusi ya fitar, inda ya ce ko kadan ba a tattaunawa wannan batu da NFF ko CAF ba.

“An dai zabi Amaju Pinnick ne a matsayin Mamba a Majalisar Hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA a zaman majalisar na 43 da aka gudanar a ranar Juma’a 12 ga watan Maris,” inji Dakta Sanusi.

Haka zalika, CAF ta gudanar da taron kwamitin zartarwa na farko a ranar Asabar bayan da Patrice Motsepe ya zamo shugaban hukumar.

A wata nasarwa da CAF ta wallafa a shafinta ta bayyana Augustin Senghor a matsayin mataimaki na daya sai Ahmed Yahya mataimaki na biyu sai Suleiman Waberi mataimaki na uku sai kuma Kanizat Ibrahim mataimaki na biyar yayin da Veron Mosengo-Omba ya zamo babban sakataren hukumar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!