Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An haifi yara sama da dubu tamanin ciki wata biyu a Kano

Published

on

  • Yawan haihuwar da aka samu a jihar Kano ya karu daga dubu sittin da tara zuwa dubu tamamin da uku daga karshen watan disamba zuwa Junairu.
  • An kuma samu raguwar mace-macen mutane a Kano.

Gwamnatin jihar Kano ta ce, yawan haihuwar da aka samu a jihar ya karu daga dubu sittin da tara zuwa dubu tamamin da uku daga karshen watan Disambar bara zuwa farkon watan junairun shekarar 2023 da muke ciki.

Daraktan kula da likitoci a hukumar kula da asibitoci jihar Kano Dakta Sulaiman Mudi Hamza ne ya bayyana hakan yayin tattaunawarsa da wakiliyar Freedom Radio, Safara’u Tijjani Adam da yake rabon magani da hukumar ta saba yi ga asibitocin jihar Kano.

Ya ce ya zuwa yanzu an samu raguwar mace-macen mutane da kananan yara a Kano, wanda hakan ke da nasaba da samun wadatattun kayayyakin kula da lafiyar al’umma.

A nata bangaren shugabar sashin bada agajin gaggawa a asibitin kwararru na Murtala Muhammad da ke Kano Hajiya Hasana Ibrahim ta ce, ‘kayayyakin na tallafawa al’umma musamman ma wadanda suka gamu da hadari’.

Hukumar kula da asibitoci ta jihar Kano ta ce, za su ci gaba da sanya idanu domin ganin kayyakin da suka bayarwa asibitocin don yin amfani da su ga al’umma.

RAHOTO:Safara’u Tijjani Adam

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!