Connect with us

Ƙetare

An kama sojojin da ake zargi da da shirya juyin mulki a Mali

Published

on

Rahotonni daga gwamnatin mulkin soji a kasar Mali sun ce, an kama sojoji kusan talatin bisa zargin su da hannu a shirin kifar da gwamnatin kasar.

 

Wasu majiyoyin tsaro sun ce waɗanda aka kama sun haɗa da Janar Abass Dembele, tsohon gwamnan yankin Mopti a tsakiyar ƙasar.

 

Kafar yada labarai ta BBC ta ruwaito cewa har zuwa lokacin da ta fitar da rahoton, gwamnatin sojin kasar ba ta ce komai ba a hukumance.

 

Haka kuma ta ruwaito cewa, Zarge-zargen yunƙurin kifar da gwamnati na nuna ƙaruwar zaman ɗar-ɗar a tsakanin gwamnatin sojin inda rahotanni ke cewa matsalar masu iƙirarin Jihadi na ƙara faɗaɗa a arewacin ƙasar ta Mali.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!