Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An karrama jami’in KAROTA saboda ƴaƙar masu ƙwacen waya

Published

on

Ƙungiyar jama’ar Arewacin ƙasar nan masu amfani da kafafen sada zumunta sun karrama wani jami’in KAROTA.

An karrama jami’in KAROTAr mai suna Abubakar Ibrahim Mukhtar ne sakamakon ƙoƙarin da yayi na cafke wasu masu ƙwacen waya a titin ɗanagundi.

Ƙungiyar ta bai wa jami’in lambar yabo da kuma kyautar kuɗi har naira dubu ɗari da goma.

Shugaban ƙungiyar Malam Ibrahim Sanyi-Sanyi ya ce, sun karrama matashin ne domin ya zama abin koyi ga na baya.

Shugaban hukumar ta KAROTA Baffa Babba Ɗanagundi ya yi godiya ga ƙungiyar inda ya ce, ita ma hukumar ta yi nisa wajen shirin karrama shi.

Haka ma ƙungiyar ta karrama Bashir Sharfaɗi na Freedom Radio da lambar yabo bisa rahoton da yayi kan matashin, wanda ya ɗauki hankulan jama’a da dama.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!