Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Buhari ya bayyana damuwar sa kan karancin malamai a makarantun kasar nan

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce malamai miliyan 1 da ake da su ba za su wadatar da adadin daliban kasar da yawansu ya kai sama da miliyan 42 ba.

Gwamnatin ta bayyana damuwarta game da karancin malamai a makarantun kasar nan, tana mai cewa akwai bukatar sake nazari akai

Shugaban hukumar bayar da ilimin bai-daya ta tarayya Dakta Hamid Boboye ne ya bayyana hakan lokacin da yake zagayen duba yadda jarrabawar tantance malamai ke gudana a birnin tarayya Abuja.

Ya ce, cikin malamai dubu 14 da suka rubuta jarrabawar a bana, malamai 3,700 ne za a dauka, wato za a dauki malamai dari-dari a ko wace Jiha sakamakon matsin tattalli arziki da ake fuskanta.

Dakta Hamid Boboye ya kuma ce akwai bukatar gwamnatocin Jihohi su tabbatar da ganin an ciyar da malaman da suka rubuta jarrabawar tantancewar gaba.

Har ma ya ce, hakan zai taimaka wajen samar da isassun malamai da za su wadatar da daliban kasar.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!