Connect with us

Labarai

An sace mutane jama’a kusan 2000 tare da kashe wasu kusan 1500 a Najeriya a 2025 NHRC

Published

on

Hukumar kare haƙƙin bil-adama ta Najeriya NHRC, ta ce, tsakanin watan Janairu zuwa Satumba na shekarar da ta gabata, an sami aukuwar sace-sacen jama’a kusan 2000, aka kuma halaka wasu kusan 1500 a sassan kasar.

 

Jami’an hukumar ne suka bayar da wannan rahoto, a wajen wani taron tuntuɓa na kuniyoyin farar hula, kan halin da ake ciki game da batutuwan da suka shafi al’amuran kare hakkin bil’adama a kasar nan a birnin tarayya Abuja.

 

Rahoton ya ce an sace mutum 1712 sannan an kashe mutum 1463 a wurare daban-daban na kasar nan, daga watan Janairu zuwa watan Satumbar.

 

Hukumar kare haƙƙin bil’adaman ta kasa ta kuma yi tsokacin, cewa an sami ƙaruwar adadin yara ƙanana da aka yi watsi da su a rariya, inda a cikin watan Satumban da ya gabata aka lissafa aukuwar hakan har sau 2723.

BBC

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!