Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An sake samun katsewar wutar lantarki a Nijeriya

Published

on

An sake samun katsewar wutar lantarki a ilahirin sassan Najeriya bayan durkushewar babbar tashar samar da wutar lantarki ta kasar a daren jiya laraba, matsalar da ke zuwa bayan TCN ta sanar da shafe akalla kwanaki 400 ta na fama da tangarda rarraba wutar lantarki a kasar mai yawan jama’a fiye da miliyan 200.

Kamfanin rarraba wutar lantarki ta Enugu EEDC ta ce ‘da misalin karfe 12 da mintuna 40 na dare ne lantarkin ya katse a tashar wanda ya jefa abokanan huldarsa a Abia da Anambra da kuma Imo baya ga jihar ta Enugu a duhu.

Haka zalika kamfanin lantarki na EKo a jihar Lagos ya sanar da katsewar wutar da misalin karfe 6 da mintuna 41 yayinda Kedco a jihar Kano ya tabbatar da wayar gari cikin duhu baya ga AEDC na Abuja.
Katsewar lantarkin na zuwa makwanni kalilan bayan kamfanin TCN ya sanar da bakar wahalar da su ke fuskanta wajen tafiyar da lantarkin kasar kari kan tulin matsalolin da bangaren na lantarkin Najeriyar ke fama da shi tsawon shekaru.
Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!