Labarai
Za a samu katsewar lantarki a Kano da kewaye – TCN

Hukumar rarraba wutar lantarki ta Najeriya TCN ta ce za a gudanar da wani aikin gyaran cibiyar raba wutar lantarki da ta shafi Kano da wasu jihohin arewacin kasar a ranar Lahadi 28 ga watan Yunin 2026.
Cikin wata sanar da daraktan ya da labaran hukumar, Ndidi Mbah ya fitar ya ce za a gudanar da gyaran domin inganta aikin rarraba wutar lantarkin.
Ya ce katsewar za ta shafi aikin rarraba wutar kamfanonin KEDCO da wasu ɓangarorin kamfanin rarraba wuta na Jos (JEDC) da na Yola (YEDC) da na Yobe (YEDC) da ke samar da wuta ga kwastominsa na Kano da Katsina da Jigawa da kuma garin Azare na jihar Bauchi.
Sauran garuruwan da matsalar za ta shafa sun haɗa da Nguru na jihar Yobe da garin Gazaoua na Jamhuriyar Nijar.
TCN ta kuma nemi afuwar al’umomin waɗannan yankuna tare da alkawarta cewa za a maida wutar da zarar an kammala aikin.
You must be logged in to post a comment Login