Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An sanya ranar rubutu jarrabawar Common Entrance

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce a ta sanya ranar 17 ga watan Okotoba a matsayin ranar da ‘yan aji shida na firamare za su rubutu jarrabawar Common Entrance a sassan kasar nan.

Wannan na kunshe cikin sanarwar da daraktan yada labarai na ma’aikatar ilimi ta kasa Ben Goong ya fitar a jiya Laraba.

Ta cikin sanarwar karamin ministan ilimi Emeka Nwajiuba ya ce jarrabawar wacce ake yin ta a rana guda zai baiwa dalibai damar shiga makarantun hadaka takasa da sauran makarantu na gwamnati da masu zaman kan su a bana.

Akan haka ne ministan ya umarci dukkanin hukumomin shirya jarrabawa da su tsara jadawalin su nan da kwanaki 7 kafin fara jarrabawar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!