Labarai
An soke jawabin da shugaba Tinubu zai gabatar ranar Alhamis

An soke jawabin da aka shirya shugaban ƙasa zai yi a safiyar yau kai tsaye gaban kafafen yaɗa labarai a wani bangare na ranar dimukradiyya.
Kwamitin shirya bukukuwan ranar Dimukuraɗiyya a Najeriya, ya bayyana cewa tun da fari an tsara shugaban ƙasa zai gudanar da jawabi a safiyar ranar Alhamis, daga bisani kuma ya gabatar da jawabin a gaban Majalisar dokoki sannan kuma ya halartar lacca a Fadar Shugaban Ƙasa da yammacin yau.
Daraktan yada Labaran shugaban kasa Tinubu, Segun Imohiosen, ya sanar da cewa shugaban kasa zai gabatar da jawabinsa kai tsaye daga cikin zauren Majalisar Dokoki a matsayin jawabin na ranar Dimukuraɗiyya.
You must be logged in to post a comment Login