Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

An ware naira biliyan uku domin gina ajujuwa a jahar Kano.

Published

on

Shugaban kwamitin ilimi a majalisar dokokin jahar Kano Muhammad Bello Butu-butu kuma wakilin ilimi na kananan hukumomin Rimin gado da Tofa a zauren Majalisa ya bayyana cewa dokar bada ilimi kyauta a Jihar nan, ya shafi kudaden da dalibai suke biya gaba daya tun daga kan makarantun firamare, har sakandire.

Muhammad Bello Butu-Butu ya bayyana hakan ne a yau jim kadan bayan kammala shirin Barka da Hantsi na nan Radio Freedom.

Ya ce jarrabawar kwalifayin da yake da a mataki uku, yanzu ya koma biyu, wanda yaci ya wuce, Wanda ya fadi ya maimaita.

Yace duk makarantar da aka kama da laifin bawa dalibai ansa yayin jarrabawa, ko kuma cin hanci da rashawa, shakka babu za’a hukuntasu dai-dai da laifinsa.

Yace idan har aka sabunta asusun tallafawa ilimi da ake sa ran kafawa, suna sa ran nan da shekara guda ma makarantun gwamnati za su sha gaban ta kudi.

 

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!