Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

An yanke wa gidan gwamnatin jihar Imo wutar lantarki

Published

on

Kamfanin rarraba wutar lantarki na shiyyar Enugu ya yanke wutar gidan gwamnatin Jihar Imo tare da Sakatariyar Jihar saboda bashin naira miliyan dari biyu da yake bi.

Mai magana da yawun kamfanin Emeka Ezah ne ya bayyana hakan ga manema labarai, ya na mai cewa ba san ran su bane maganar ta je kafofin yada labarai, sai dai dan barazanar ruguje ginin kamfanin da gwamnatin jihar Imo tai musu.

Emeka ya kuma ce ana ta kokarin yadda za’a shawo kan matsalar har gwamnatin ta biya kudaden.

A ta bakin Emeka kin biyan kudin wutar da masu ruwa da tsaki ke yi, ka iya haifar da matsaloli tsakanin kamfanin da talakawan gari.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!