Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisa: akwai bukatar sake nazarin kundin tsarin kasa

Published

on

Majalisun dokokin kasar nan sun ce akwai bukatar sake nazartar kundin tsarin mulkin kasar nan ta yadda zai bada damar samar da ‘yan sandan jihohi, wanda majalisun ke ganin cewa zai kawo karshen rigingimu da kashe kashen da ke faruwa a sassan kasar nan.

Bukatar ta zo ne a zaman majalisun na jiya, inda suka ce tsarin harkokin tsaron kasar nan ya gaza, a don haka akwai bukatar a baiwa jihohin kasar nan damar kafa ‘yan sandan su.

Majalisun biyu sun amince da a sake nazartar kundin tsarin mulkin kasar nan domin cimma wannan manufa.

Bukatar sake nazartar kundin tsarin mulkin na zuwa ne bayan da wasu ‘yan bindiga da ba’a san su ba suka harbe wasu ‘yan sanda 7 har lahira a daren ranar Litinin din da ta gabata a birnin Tarayyar Abuja .

Tuni majalisun suka kafa kwamitin da zai nazarci kundin tsarin mulkin wanda mataimakin shugaban majalisar dattijai Ike Ekweremadu zai jagoranta tare da gabatar da rahoton su cikin makwanni 2.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!