Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Za a ɗaga matsayin tashar wutar lantarki ta jihar Yobe

Published

on

Gwamnatin tarayya za ta ɗaga matsayin tashar wutar lantarki ta jihar Yobe ta yadda wuta za ta wadaci al’ummar jihar.

Ministan lantarki na ƙasa Injiniya Abubakar Aliyu ne ya bayyana hakan ranar Labara yayin ziyarar gani da ido a babbar tashar lantarki ta jihar Yobe da ke Damaturu.

Ministan wanda ya samu wakilcin Injiniya Sule Abdulazeez shugaban kamfanin raba wutar lantarki na kasa TCN, ya ce za a ɗaga matsayin tashar ne, domin ƙaruwar buƙatarta ga al’umma.

Ya ce “An bada kwangilar samar da na’urar da za ta ƙara yawan wutar lantarki mai karfin Volt-Amps (MVA) miliyan 150 a wannan tasha”.

Injiniya Abubakar Aliyu ya yabawa hukumomin tsaro saboda ƙoƙarinsu wajen samar da tsaro ga tashar wutar lantarkin.

Ministan yayi kira ga jama’ar da ke kusa da tashar lantarkin da su riƙa sanya idanu game da ita.

A watan Fabrairun shekarar 2019 ne Shugaba Muhammadu Buhari ya ƙaddamar da tashar wutar lantarkin ta Damaturu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!