Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

An yi jana’izar daliban da suka rasa rayukansu a wani hatsari a jihar Kano

Published

on

Da maraicen jiya ne aka gudanar da jana’izar daliban nan ashirin da daya da malaman su uku wadanda suka rasa rayukan su a wani hatsarin mota da ya ritsa da su a yankin karamar hukumar Gaya da ke nan jihar Kano.

 

Rahotanni sun ce an gudanar da jana’izar daliban ne a fadar Sarkin Misau da ke garin na Misau a jihar Bauchi.

 

Kamfanin dillancin labarai na kasa NAN ya ruwaito cewa dubban mutane ne suka halarci jana’izar wanda limamin babban masallacin juma’a na garin Misau Sheikh Usman Baba ya jagoranta.

 

Daliban dai sun rasa rayukansu ne a jiya sakamakon wani mummunar hatsarin mota da ya ritsa da su a yankin karamar hukumar Gaya lokacin da suke komawa gida bayan kammala wata ziyarar karin ilimi da suka kawo nan jihar Kano wato Excursion.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!