Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Gwamnatin tarayya ta ce ta baiwa jihohin kasar nan tallafin tiriliyan daya a shekaru biyu

Published

on

Gwamnatin tarayya ta ce jihohin kasar nan talatin da shida sun karbi tallafin sama da naira tiriliyan daya daga wajen gwamnatin tarayya tsakanin shekarar dubu biyu da sha biyar zuwa shekarar da ta wuce.

Mataimakin shugaban kasa farfesa Yemi Osinbajo ne ya bayyana haka ga manema labarai jiya a garin Lokoja babban birnin jihar Kogi.

Ya ce kudaden sun hada da: tallafin kasafin kudi da kudaden Paris club da kudaden rarar man fetur da dai sauransu.

Farfesa Yemi Osinbajo wanda ke jawabin a wajen taron saka hannayen jari da tattalin arziki wanda gwamnatin jihar Kogi ta shirya ya ce, an baiwa jihohin kudaden ne domin ba su damar gudanar da ayyukan raya kasa.

Mataimakin shugaban kasar ya ce mafi yawa daga cikin kudaden mallakin jihohin ne wadanda aka dawo musu da shi daga kungiyar ba da lamuni ta Paris club da kuma kudaden rarar man fetur.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!