Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

An yi jana’izar matukin jirgin yakin sojin sama da yi yi hatsri

Published

on

An yi jana’izar matukin jirgin yakin rundunar sojojin sama na kasar nan Bello Muhammed Baba-Ari wanda ya rasa ransa sakamakon taho mu gama da wasu jirage da ke atisaye suka yi a jiya Juma’a.

Squadron leader Bello Muhammed Baba-Ari yana daya daga cikin matuka jirage uku da hatsarin ya ritsa da su a tsaunin Katamkpe da ke birnin tarayya Abuja.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai magana da yawun rundunar sojojin sama na kasar nan Air Commodore Ibikunle Daramola.

Sanarwar ta kuma ruwaito babban hafsan sojojin sama na kasar nan Air Marshall Sadique Abubakar na bayyana marigayin a matsayin jarumin soja da ya taka a bakin daga.

Ya kuma yi addu’ar Allah ya gafar ta masa ya kuma bai wa iyalansa hakurin jure rashi.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!