Connect with us

Labarai

An yi watsi da bukatar ma’aikata yayin tsara dokar Haraji – NLC

Published

on

Shugaban Kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC), Comrade Joe Ajaero, ya bayyana damuwa kan sabuwar dokar haraji, yana mai cewa an yi watsi da bukatar ma’aikata yayin tsara dokar, lamarin da ya kara nauyi ga masu karamin karfi. Ya ce harajin da ya shafi albashin mafi karanci ba adalci ba ne kuma yana tilasta wa talakawa karin nauyi.

Ajaero ya gargadi gwamnati da kada ta cigaba da aiwatar da dokar ba tare da gyara ba, yana mai cewa ci-gaba da hakan zai iya rage amincewar jama’a da kawo barazana ga tsarin dimokuradiyya. Ya ce dokar tana nuna cewa ma’aikata da talakawa sun kasance a waje yayin yanke hukunci mai tasiri a rayuwarsu.

Ya kuma jaddada cewa dimokuradiyya ba ta tsaya ga zabe kawai ba; tana bukatar mutunta doka, inganta hukumomi, da gwamnati mai hidima ga al’umma baki daya. Ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta sake duba dokar domin tabbatar da adalci ga kowa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!