Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Ana iya daukar cutar Corona ta iska – WHO

Published

on

Hukumar lafiya ta duniya WHO ta ce akwai shaidun dake nuna cewar ana iya daukar cutar Covid-19 ta iska, sakamakon binciken da wasu masana kimiyya suka yi, wanda ke nuna cewa kwayar cutar na iya tafiya fiye da minti biyu a iska kafin ta fadi.

Babbar Jami’a a hukumar Farfesa Benedetta Allgranzi ce ta sanar da wannan sabon rahoto, inda ta ce sun tabbatar da wannan sabon binciken, saboda haka yana da muhimmanci mutane su fahimci wannan sabon bincike domin kiyaye wa.

Binciken da masana kimiyar 239 suka yi a duniya, ya ce cutar na iya tafiya fiye da mita biyu, lokacin da wanda ya kamu da ita ya numfasa ko kuma ya zubar da wani ruwa daga jikin sa.

Kafin wannan lokaci dai, hukumar ta ce ana yada wannan cutar ne sakamakon mu’amala tsakanin mai dauke da ita, abinda ya sa aka bukaci bayar da tazarar akalla mita biyu tsakanin jama’a wajen hulda yau da kullum.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!