Connect with us

Labarai

APC ce za ta lashe zaɓen ƙananan hukumomi baki ɗaya – Ganduje

Published

on

Gwamnan Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya ce, In Allah ya yarda jam’iyyar APC ce za ta cinye zaɓen baki ɗaya.

Ganduje ya bayyana hakan ne, jim kaɗan bayan da ya kaɗa ƙuri’arsa a mazaɓarsa.

A cewar sa, la’akari da yawan fitowar jama’a na nufin jam’iyya mai mulki zata lashe dukkan kujerun.

Ganduje ya kuma ce, an gudanar da zaɓen cikin tsari me kyau.

Zuwa yanzu dai an fara tattara sakamakon zaɓe a wasu mazaɓun bayan da aka kammala kaɗa ƙuri’a.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!