Connect with us

Labarai

APC ta bayyana ranar gudanar da taron Kwamitin Zartaswarta

Published

on

Jam’iyyar APC, mai mulki ta bayyana cewa za ta gudanar da taron Kwamitin Zartaswarta na Kasa NEC a ranar 24 ga watan nan da muke ciki na Yuli, domin zaɓen wanda zai maye gurbin tsohon Shugaban jam’iyyar na ƙasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje.

 

jam’iyyar, ta bayyana hakanne ta cikin wata sanarwa da ta fito daga Mataimakin Sakatarenta na ƙasa Festus Fuanter, bayan kammala taron Kwamitin Gudanarwar Jam’iyyar NWC karo na 174.

 

Festus Fuanter ya ƙara da cewa an riga an aika takardar sanarwar taron zuwa Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta INEC, kamar yadda doka ta tanada.

 

A cewar jam’iyyar, taron kwamitin zartaswar zai mayar da hankali kan cike gurbin shugaban jam’iyyar, wanda ya zama wajibi sakamakon saukar Dakta Ganduje daga wannan matsayi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!