Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

PDP:Ta Kira taron gaggawa don tauna batutuwan zabe

Published

on

Jam’iyyar PDP ta kira wani taron gaggawa domin tattana batun dage zabukan kasa da hukumar zabe ta kasa INEC ta yi a makon jiya.

Taron wanda ake saran za a gudanar da shi yau Talata a birnin tarayya Abuja, shugaban jam’iyyar na kasa Uche Secondus ne zai jagoranta.

Mai Magana da yawun jam’iyyar Mr Kola Ologbondiyan, ya ce za a gudanar da taron ne domin sake nazartar shirye-shiryen da jam’iyyar ta yi kan zabukan kasa.

A cewar sa kwamitin gudanarwar jam’iyyar ne zai gudanar da taron a sakatariyar jam’iyyar da misalin karfe goma sha biyu na ranar yau.

Haka zalika ya kara da cewa shugabannin jam’iyyar za su kuma tattauna kalaman da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi kan masu satar akwatunan zabe a yayin taron kwamitin gudanarwar jam’iyyar APC jiya a Abuja.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!