Connect with us

Siyasa

APC ta zabi sabbin shugabannin ta na kasa

Published

on

Jam’iyyar APC mai mulkin kasa ta zabi sabbin shugabanninta na kasa a taron da ta gudanar a Eagle Square da ke babban birnin tarayya Abuja inda Farfesa Nentawe Yilwatda ya zama sabon Shugaban jam’iyyar, yayin da Sanata Surajudeen Basiru ya zama Sakataren ta kasa.

 

Sauran mukaman da aka cike sun hada da mataimakan shugabanni na Arewa da Kudu, sakatare da mataimakinsa, mai kula da harkokin kudi, mai tsare-tsare, da kakakin jam’iyya da sauransu. Haka kuma an zabi shugabannin mata, matasa da masu bukata ta musamman.

 

Manyan jagororin jam’iyyar sun halarci taron, ciki har da Shugaba Bola Tinubu, Mataimakin Shugaba Kashim Shettima, Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio da Kakakin Majalisar Wakilai Tajudeen Abbas, tare da wakilai daga sassa daban-daban na kasa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!