Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Arsenal ta yi rashin nasara a hannun Manchester City

Published

on

Bayan dawowa, gasar firimiyar kasar Ingila, sakamakon tsaikon da ta samu akan cutar Corona tun watan Maris kungiyar Arsenal, ta fara gasar da koma baya, bayan ta sha duka a hannun Manchester City.

Wasan wanda ya gudana a yau, Raheem Sterling ne ya fara saka Manchester City a gaba a minti na 45, ana dab da za a tafi hutun rabin lokaci.

Ya yinda jim kadan bayan dawowa, dan wasan Arsenal David Luiz, ya samu katin kora na ja, a minti 49, sakamakon kayar da Riyard Mahrez a cikin da’ira ta 18, an kuma karawa Arsenal kwallo ta biyu a minti na 51, ta bugun daga kai sai mai tsaron gida da Kevin De Bruyne yayi sakamakon ketar da David Luiz yayi.

Kwallo ta uku, matashin dan wasa Phil Foden ne ya zura ta a minti na 90 ana dab da a tashi wasa.

Arsenal na dakon nasarar ta ta farko bayan dawowa daga hutun, ya yin da zata karbi bakuncin Brighton and Hove Albion, ya yin da Manchester City zata karbi bakuncin Burnley.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!